MINISTAN WASANNI YA ZIYARCI KADUNA

Farfesa tauheed Adedoja,sabon ministan wasanni kuma shugaban hukumar wasanni ta kasa (NSC).Yace za’a baiwa jihar Kaduna muhimmanci tare da kulawa na musamman lokacin da gwabnatin tarayya ta soma gina kananan filayen wasanni a karkara a yunkurin ta na habbaka wasanni a matakin karkara.
Ministan ya bayyana hakan ne a karshen zirar gani da ido da ya kai fililayen wasanni dake Ahmadu Bello Kaduna ranar jumma’a.
Ya kuma yi alkawari inganta darajar dakunan kwanan yan wasa (hostel) domin maida shi otel kafin watan mayun wannan shekarar tare da umurni cewa a saka sunayen yan wasan da sukayi fice daga bangaren kassan a kofar dakuna otel bayan da aka kamala.
Farfesa Adedoja ya ziyarci filayen wasanni tanis,kwallon raga,kwallon bango,kwallon kafa da wajen ninkaya da dai sauran su.

No comments:

Post a Comment